Za a yi jana'izar Kofi Annan ranar 13 ga watan Satumba - arewastar arewastar: Za a yi jana'izar Kofi Annan ranar 13 ga watan Satumba

Pages

Featured Featured
how-to-use-your-android-device-as
Techwise Blogger Template By 24clan Team
dent-free-data
Liberty 3 Column Blogger Template By 24clan Team
9mobile-special-offer
Publisher V7.5.1 Premium - WordPress News Template By 24clan Team
mtn-double-data-cheat
Sahifa v5.6.10 Premium Wp Theme By 24clan


Saturday, August 25, 2018

Za a yi jana'izar Kofi Annan ranar 13 ga watan Satumba


Shugaban kasar Ghana Nana Akufo Addo ya ce za a yi wa tsohon shugaban majalisar dinkin duniya Mr Kofi Annan jana'izar ban-girma.

Mr Annan, wanda dan asalin kasar Ghana ne, ya mutu ranar Asabar din da ta gabata a birnin Geneva, inda ya kwashe shekara da shekaru yana zaune da iyalinsa.

Mr Addo ya bayyana haka ne lokacin da wata tawagar mutum bakwai na iyalan tsohon babban jami'in diflomasiyyar ta ziyarce shi a gidan gwamnatin kasar da ke Accra.

Tsohon shugaban majalisar dinkin duniya Kofi Annan ya rasu

Duniya na alhinin mutuwar Kofi Annan

A cewar sa, za a yi wa Mr Annan jana'izar ban-girma ranar 13 ga watan Satumba a matsayinsa na babban ma'aikacin diflomasiyya da kuma dan kasar na gari.

Ya kara da cewa gwamnatin Ghana ce za ta dauki nauyin dukkan abubuwan da za su faru lokacin jana'izar.

Shugaban kasar ta Ghana ya ce shugabannin kasashe da dama sun kira shi inda suka yi masa ta'aziyyar mutuar Mr Annan, yana mai cewa yana sa ran da dama daga cikin su za su halarci jana'izarsa.



Copy the link below and Share with your Friends:

Download Our Official Android App on Google Playstore HERE
OR
Download from another source HERE



No comments:

Post a Comment