BBC News Hausa 2019: An sanya ranar zaben shugaban kasar Nigeria - arewastar arewastar: BBC News Hausa 2019: An sanya ranar zaben shugaban kasar Nigeria

Pages

Featured Featured
how-to-use-your-android-device-as
Techwise Blogger Template By 24clan Team
dent-free-data
Liberty 3 Column Blogger Template By 24clan Team
9mobile-special-offer
Publisher V7.5.1 Premium - WordPress News Template By 24clan Team
mtn-double-data-cheat
Sahifa v5.6.10 Premium Wp Theme By 24clan


Sunday, December 10, 2017

BBC News Hausa 2019: An sanya ranar zaben shugaban kasar Nigeria


Hukumar zaben Najeriya (INEC) ta sanya ranar da za a yi zaben shugaban kasa na shekarar 2019, inda za a yi zaben nan da kwana 433 masu zuwa.
Shugaban Hukumar Farfesa Mahmood Yakubu ya ce, a ranar 16 ga watan Fabrairun 2019 ne za a yi zaben shugaban kasar da 'yan majalisar tarayya.
Yayin da ranar 2 ga watan Maris na shekarar 2019 za a yi zaben gwamnoni da 'yan majalisar jiha, da kuma zaben shugabannin kananan hukumomin babban birnin Najeriya Abuja.
Yakubu ya bayar da sanarwar ne ranar Juma'a a wani taro da huhumar ta gabatar a Uyo, babban birnin jihar Akwa Ibom.
"Duk wadanda suka halartaci taron nan ya kamata su san cewa daga yau (Juma'a) saura kwana 434 a gudanar da babban zaben shekarar 2019, wato ranar 16 ga watan Fabrairu inda za a fara da zaben shugaban kasa da na majalisar tarayya," in ji shi.
Ya kara da cewa, sababbin masu kada kuri'a kimanin 3,630,529 aka yi rijista, kuma za a ci gaba da yin rijistar har zuwa kwana 60 kafin babban zaben.
A kalla jam'iyyu 67 ne suka nuna sha'awarsu ta shiga zaben, har ila yau hukumar ta karbi takardar masu neman yin rijista fiye da 120 daga kungiyoyin siyasa da suke neman a yi musu rijista a matsayin jam'iyya.



Copy the link below and Share with your Friends:

Download Our Official Android App on Google Playstore HERE
OR
Download from another source HERE



No comments:

Post a Comment