PDP ta yi kawance da jam'iyyu 40 'don doke Buhari' - arewastar arewastar: PDP ta yi kawance da jam'iyyu 40 'don doke Buhari'

Pages

Featured Featured
how-to-use-your-android-device-as
Techwise Blogger Template By 24clan Team
dent-free-data
Liberty 3 Column Blogger Template By 24clan Team
9mobile-special-offer
Publisher V7.5.1 Premium - WordPress News Template By 24clan Team
mtn-double-data-cheat
Sahifa v5.6.10 Premium Wp Theme By 24clan


Monday, July 9, 2018

PDP ta yi kawance da jam'iyyu 40 'don doke Buhari'

Babbar jam'iyyar adawa a Najeriya PDP ta kulla wani sabon kawance da wadansu jam'iyyu fiye da 40 da ke kasar, gabanin babban zaben shekarar 2019.
Jam'iyyun sun sanar da hakan ne lokacin wani taro da suka yi a Abuja ranar Litinin, inda suka yi wa kawance lakabi da Coalition of United Political Parties (CUPP).
Sanarwar ta biyo bayan sanya hannu kan wata yarjejeniya da suka cimma da shugabannin jam'iyyun,"don kayar da Shugaba Muhammadu Buhari a zaben 2019," a cewarsu
Yarjejeniyar ta kunshi wani shiri ta yadda za su tsayar da dan takara daya tilo a zaben shugaban kasa, da na gwamnoni a jihohi da kuma kujerun majalisa.
Sai dai zuwa yanzu jam'iyya mai mulki ta APC ba ta mayar da martani ba, game da batun.
Cikin wadanda suka halarci taron har da shugaban sabuwar jam'iyyar APC Injiniya Buba Galadima da kuma mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa Ike Ekweremadu da sauransu.
A shekarar 2015 ne jam'iyyar APC ta doke PDP a babban zaben kasar, bayan ta shafe shekara 16 tana mulkin kasar.


Copy the link below and Share with your Friends:

Download Our Official Android App on Google Playstore HERE
OR
Download from another source HERE



No comments:

Post a Comment