Gwamnonin Nigeria sun amince a kashe $1bn don yaki da Boko Haram - arewastar arewastar: Gwamnonin Nigeria sun amince a kashe $1bn don yaki da Boko Haram

Pages

Featured Featured
how-to-use-your-android-device-as
Techwise Blogger Template By 24clan Team
dent-free-data
Liberty 3 Column Blogger Template By 24clan Team
9mobile-special-offer
Publisher V7.5.1 Premium - WordPress News Template By 24clan Team
mtn-double-data-cheat
Sahifa v5.6.10 Premium Wp Theme By 24clan


Wednesday, December 20, 2017

Gwamnonin Nigeria sun amince a kashe $1bn don yaki da Boko Haram

Gwamnonin Jihohi 36 sun tattauna matsalar tsaro da karancin Fetur
Gwamnonin jihohin Najeriya sun goyi bayan a kashe kudi dala biliyan daya domin yaki da kungiyar Boko Haram a arewa maso gabashin kasar.
Gwamnan Jihar Zamfara Abdul'aziz Yari shugaban gwamnonin jihohin kasar 36 ne ya sanar da matakin a taron majalisar zartarwa da aka gudanar, wanda Farfesa Yemi Osibanjo ya jagoranta a fadar shugaban kasa a Abuja.
Gwamnan Jihar Edo Godwin Obaseki ya shaidawa manema labarai cewa gwamnonin sun amince gwamnatin Tarayya ta kashe kudi dala biliyan daya domin yakar Boko Haram.
Za a dai kashe kudaden ne daga asusun rarar kudin mai na kasar.
Gwamnonin sun ce sun amince a kashe kudaden ne saboda ci gaban da aka samu a yaki da Boko Haram.
Boko Haram dai na ci gaba da zama barazana a arewa maso gabashin kasar, inda mayakan kungiyar ke ci gaba da kai hare-haren kunar bakin wake tare da kashe fararen hula.
Gwamnonin kuma sun tattauna matsalar karancin fetur da ake fuskanta a sassan Najeriya, inda karamin ministan albarkatun mai ya yi alkawalin cewa za a kawo karshen matsalar nan da sa'o'i 48.
Har yanzu ana fama da dogayen layi a gidajen mai a manyan biranen Najeriya, kasar da ta fi arzikin mai a nahiyar Afirka.


Copy the link below and Share with your Friends:

Download Our Official Android App on Google Playstore HERE
OR
Download from another source HERE



No comments:

Post a Comment